Gwamnatin jamhuriyyar kasar Nijer ta mika sakon ta’aziyyarta ga Farfesa Adamu Abubakar-Gwarzo, shugaban Jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN) dake garin Maradi a jamhuriyyar Nijer bisa rasuwar daya daga cikin jajirtattun Malaman jami’ar.
Sakon ta’aziyyar na dauke ne a cikin takardar da ministan manyan makarantu na Nijer din, , Malam Yahuza Salisu Madobi ya sanyawa hannu ya kuma aiko wa Farfesa Gwarzo, shugaban jami’ar MAAUN din, inda shi kuma ya rabawa ‘yan jarida a Kano a ranar Litinin.
Ministan ya bayyan kaduwarsa bisa rasuwar Malam Jamilu Sambo, inda ya bayyana rasuwar marigayin a matsayin rashi babba da aka yi ba kawai ga iyalinsa ba har ga jami’ar, jamhuriyyar Nijer da ma Afrika baki daya.
“Gwamnatin jamhuriyyar Nijer da dukkanin ma’aikatan dake karkashin ma’aikatar ilimin manyan makarantu muna mika sakon ta’aziyyarmu da alhininmu ga hukumar gudanar da wannan jami’ar da ma’aikatanta da dukkanin al’ummar Jami’ar baki daya bisa rasuwar daya daga cikin Malaman makarantar, Malam Jamilu Sambo.” Inji sanarwar.
Ministan ya yi addu’ar Allah ya jikan Marigayi, ya kuma bai wa iyalansa da ma jami’ar baki daya dangana da hakuri, tare da kuma hakurin jure wannan rashin da aka yi.
Marigayi Jamilu Sambo ya rasu yana da shekara 54 a duniya. Kuma kafin rasuwarsa Malami ne a sashen sanin halayyar dan Adam na Jami’ar MAAUN. Kuma ya rasu ya bar mata daya da kuma ‘ya’ya hudu.