Shugaban hukumar kula da lafiya a matakin farko ta Jihar Bauchi, dakta Rilwanu Mohammed ya ce hukumar ta tabbatar da bullar cutar ta kyandae buri a karon farko.
Mohammed ya shaidawa manema labarai ranar Juma’ar nan a Bauchi cewa akwai wasu mutane biyu da ake zargi ya yin da ake bincike.
“An gano mutum daya yana dauke da cutar yayin da wasu biyu kuma ake duba su.
KARANTA WANNAN: https://dimokuradiyya.com.ng/rundunar-yan-sandan-kano-shiyya-ta-1-ta-karyata-labarin-yan-taadda-sun-yi-luguden-wuta-a-hedkwatar/
“Majinyacin ya fito ne daga Adamawa kuma a halin yanzu yana samun kulawa a daya daga cikin cibiyoyin kula da lafiya da ke jihar.
” Ba za mu bar shi ya tafi ba har sai mun gamsu da yanayinsa don kada ya cuci wasu.
Ya kara da cewa, “Ba kamar kwalara ba inda za ka jira kimanin mutane 15 kafin ka bayyana bullar cutar, tare da tabbatar da bullar cutar guda daya ta kyandar buri,” in ji shi.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Sai dai ya tabbatar wa jama’a cewa hukumar tare da hadin gwiwar kungiyoyin raya kasa na kokarin dakile yaduwar cutar.
Mohammed ya ci gaba da bayanin cewa an kara sa ido don ganin an yi maganin wadanda ake zargi da ita nan take.
Ya yi kira ga jama’a da su duba alamun cutar domin samun ingantaccen tsarin kula da lafiya.
Mohammed ya lissafa alamomin da suka haɗa da: zazzaɓi, ciwon kai, kai-kayi da ciwon baya, kumburin ƙwayoyin lymph; sanyi da gajiya.
Ya lissafta wasu kamar haka: alamomin numfashi da kurji mai iya kama da pimples ko blisters da ke fitowa a fuska, cikin baki da sauran sassan jiki.
(NAN)