Hukumar tattara haraji ta jihar Kaduna (KADIRS), tace gwamantin jihar ta shirya tsaf domin kulle dukkanin tashoshin mota da suke jihar wanda ba bisa ƙa’ida, domin bunƙasa harkar tattara haraji a jihar Kaduna.
Shugaban hukumar Zaid Abubakar ne, ya bayyana haka a yayin tattaunawarsa da manema labarai a yau Asabar.
Abubakar ya ƙara da cewa hukumomin da suke da alhakin da ya shafi harkar sufuri na jihar zasu fara rangadin rufe tashoshin daga sati mai zuwa.
“Sati mai zuwa za a fara rufe tashoshin da suke ba bisa ƙa’ida ba, kuma hukumomin da suke da ruwa tsaki su ne zasu gudanar wannan aiki, sannan za a kawo sabon tsarin tattara haraji,” inji Abubakar.
“A halin da muke ciki yanzu bama samun harajin da ya kamata daga tashoshin saboda ba bisa ƙa’ida suke ba”.
“Rufe tashoshin zai taimakawa tsarinmu na tattara haraji”.
Kamar yadda ya bayyana cewa hukumar tara haraji ta jihar zata ci gaba da tabbatar da cewa duk wasu masu Kasuwanci sun biya harajinsu ga gwamnatin jihar.
Abubakar ya shawarci masu biyan haraji da su ci gaba da biyan haraji domin ta haka ne gwamnati zata samu damar samar da ayyukan da suka shafi tsaro, ci gaban al’umma da sauran ababen more rayuwa.