Majalisar dokokin Kano ta amince da korar wasu ma’aikatan hukumar lura da ayyukan majalisar dokokin Kano, mutum Uku.
Mukaddashin gwamnan Kano Nasiru Yusuf Gawuna, ne ya aikewa majalisar sunayen mutanen uku don ta amince da korar su.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa, gwamnatin ta kori ma’aikatan ne bayan samun su da rashin gudanar da ayukan su yadda ya kamata.
Shugaban masu rinjaye na majalisar Dokokin Labaran Abdul Madari, ya ce dokar hukumar ta baiwa gwamna dama a sashi na biyar sakin layi na daya idan aka samu wani da rashin yin abinda ya dace ko laifi ya rubutowa majalisar don amincewa da sallamar su idan aka samu kaso daya bisa uku na yan majalisar suka goyi bayan hakan.
Ya ce za a maye gurbin wadanda aka kora da wasu da suka fito daga yankunan da suke.