A wani yunƙuri da take yi na ƙoƙarin magance matsalar ‘yan bindiga da suka addabi sassan jihar, gwamnatin Katsina ta ce ta ɓullo da wani sabon tsarin yaƙi da wannan matsala ta tsaro da ta ƙi ci ta ƙi cinyewa.
Gwamnatin jihar Katsina, ta ce tana shirin fara aiwatar da wani sabon tsari da zai taimaka wajen yaƙi da matsalar ‘yan bindiga da ke kai hare-hare a wasu sassan jihar.
Yayin wata hira da ya yi da Muryar Amurka, shugaban kwamitin tsaro a jihar Dakta Mustapha Inuwa, ya ce za a raya dajin da ya zama maɓuya ga ‘yan bindigar.
A cewar Inuwa, ɗaukan wannan mataki zai “ta da dajin daga mafakar waɗanda suke amfani da hanyar suna shiga garuruwan Babban Duhu, Lamma, Kurfi da sauran su.
An yake “shawarar cewa, dajin nan a maida shi gonaki, kuma waɗanda suke sha’awa a yanka masu su yi gidaje a wurin daga ƙarshe kuma gwamnatin ta fara yin makaranta da asibiti.” In ji Dakta Inuwa.
https://dimokuradiyya.com.ng/sojoji-sun-kashe-yan-bindiga-100-a-yankin-katsina-da-zamfara/
A cewarsa, tuni gwamnati ta ba da umurnin a fara aiki a dajin domin a kawar da manyan itatuwa.
Za a maida dazukan da maharan ke ɓoyewa ya zama filaye da gonakin noma ne ga maharan da suka tuba ga kuma jama’ar da suka nuna sha’awarsu.
Shugaban kwamitin tsaron ya ƙara da cewa, har yanzu ƙofar yafiya ga maharan a buɗe take illa dai tsarin ya koma hannun sojojin Najeriya.
Wasu daga cikin jama’ar yankin da lamarin zai shafa, sun yi fatan ɗorewar wannan tsari da ake ƙoƙarin shimfiɗawa wanda suka ce ya yi daidai idan har zai kawo sulhu da maharan.
Jihar Katsina ta jima tana fama da matsalar ‘yan bindiga a ‘yan shekarun nan lamarin da ya yi sanadin mutuwar ɗaruruwan mutane tare da asarar dumbing dukiyoyi.