Majalisar zartarwa ta jihar Nasarawa ta amince da kafa ma’aikatar raya karkara a jihar domin kawo ci gaba da wasu yankuna dake jihar.
Ana sa ran dai sabuwar ma’aikatar za ta riƙa gudanar da dukkannin ayyukan raya ƙasa a yankunan karkara da suka haɗa da samar da hanyoyi, wutar lantarki da kuma ruwan sha.
Kwamishinan yaɗa Labarai, Al’adu da Yawon Bude Ido na jihar, Dogo Shammah shi ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga manema labarai tare da ƙarin bayani jim kaɗan bayan kammala taronsu majalisar na wata-wata.
https://dimokuradiyya.com.ng/gwamnan-jihar-nassarawa-ya-sallami-sakataren-gwamnati-daga-aiki/
Ya ce hukumar za kuma ta fara aikin ginawa da kula da ƙananan hanyoyi tare da inganta su tare da aikin samar da ruwan sha a duk faɗin jihar.
Har wa yau, kwamishinan ya ce gwamnatin jihar ta amince cewa daga yanzu tilas ɓangarori, ma’aikatu da hukumominta su riƙa tattara bayanai ta hanyar sabuwar fasahar sadarwa domin tafiya da zamani.
Kwamishinan ya ce hakan na cikin ƙudirin da gwamna Abdullahi Sule yake da shi na ganin cewa jihar ta shiga sahun jihohi uku a Najeriya da baƙi masu yawon buɗe ido ke sha’awar zuwa a Najeriya.