Gwamnatin jihar Oyo ta sassauta dokar kulle da kuma bude makarantu a jihar.

Gwamnatin jihar Oyo ta sassauta dokar kulle da ta saka don dakile yaduwar cutar sarke numfashi a jihar.

Gwamnati ta ce daga ranar 29 ga watan Yuni da muke ciki, duk ma’aikatan jihar  su dawo bakin aikinsu.

” Sannan kuma yaran makarantu daga aji 6, JSS 3, SS 3 su dawo domin ci gaba da karatu.”

Sakataren yada labarai na jihar Taiwo Adisa ne, ya sanar da haka a takarda da ya raba wa manema labarai ranar Litini. Sannan muatne za su ci gaba da walwala tun daga karfe 4 na asuba zuwa 10 na dare.

Ya kuma ce wuraren ibada a jihar za su ci gaba da ibada kamar yadda aka saba a da sai dai kuma za a bi ka’idojin da gwamnati ta saka na kariya daga kamuwa da Korona.

Idan ba a manta ba gwamnatin  jihar ta amince wa ma’aikata daga mataki na 13 zuwa sama, da su fara zuwa aiki tun a ranar 27 ga watan Afrilu. Amma yanzu gwamnati ta bude duk ofisoshi domin duk ma’aikatan su dawo bakin aikinsu a Litini 22 ga watan Yuni.

“Duk daliban da gwamnati ta amince su fara karatu za su saka takunkumin fuska, wanke hannaye da amfani da man tsaftace hannaye.

Next Post

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Archives

Welcome Back!

Login to your account below

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.