Gwamnatin jihar Zamfara ta ɗauki ma’aikatan lafiya 282 da kuɗin ma’aikatan bogi 93 dake jihar.
Shugaban harkokin asibiti na jihar Alhaji Mustafa Anka ne ya bayyana hakan biyo bayan binciken ƙwaƙwaf da hukumar tasu ta gudanar.
Ya ƙara da cewa duk wata gwamnatin jihar na biyan Miliyan 23 ga Likitocin bogi.
Anka yace gwamna Matawalle ne ya bashi umarnin sake ɗaukar wasu ma’aikatan lafiya har 282 da kuɗin dake biyan Likitocin bogin.
Ya ce “mun ɗauki ma’aikatan lafiya na fanni daban-daban har guda 282 domin maye wancan gurbin”.