Gwamnatin jihar Kano ta ayyana ranar Litinin a matsayin ranar hutun aiki, domin murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci, ta 1444H.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai Malam Muhammad Garba ya fitar a Kano.
“ Don haka gwamna Abdullahi Ganduje yana taya al’ummar musulmin jihar murna kan muhimmancin bikin sabuwar shekarar ya kuma bukaci a taimakawa kai.
“Ya kuma yi kira gare su da su yi amfani da wannan hutun wajen neman gafarar Allah, da kuma yi musu addu’a domin ceto al’umma daga matsalolin tsaro da ke addabar kasar,” inji shi.
Ya kuma tabbatar wa mazauna jihar a shirye gwamnatinsa ta ke da su ci gaba da cika alkawarin da ta dauka na inganta rayuwarsu ta hanyar aiwatar da shirye-shirye da ayyuka da suka shafi mutane.
Gwamna Ganduje ya kuma bukaci wadanda har yanzu ba su karbi katin zaben su ba, da su yi hakan, domin ba su damar yin amfani da katin zabe a zabe mai zuwa.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Muharram shine watan farko na kalandar Musulunci, kuma ana daukarsa a matsayin wata mai alfarma bayan Ramadan.
Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya rawaito cewa mai alfarma sarkin musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III ya umurci al’ummar musulmi da su fara duban jinjirin watan Al-Muharram daga ranar Alhamis, wanda yayi daidai da ranar 29 ga watan Zul-Hijjah shekara ta 1443 bayan hijira.
Musulman duniya sun yi amfani da shi wajen gudanar da al’amuran Musulunci da muhimman ranakun Musulunci.
Dukkanin ranaku a kalandar Musulunci ta 2022 sun dogara ne akan ganin watan kasar.
(NAN)