Gwamnatin jihar Kano ta ce akalla almajirai 193 ne suka kamu da cutar korona a fadin jihar, lamarin da ya haifar da damuwa game da mayar da almajirai jihohinsu.
Kwamishinan ilimi Sunusi Muhammad Kiru ne ya bayyana hakan. Ya ce an kwashe akalla almajirai 1,500 daga jihar Kano zuwa jihohinsu, ita kuma Kano aka dawo mata da guda 400.
Kwamishinan ya ce, lokaci ya wuce da alarammomi za su ci gaba da kwaso almajirai da ba su ma san inda almajiran suke kwana ba.
Ya ce don haka wajibi ne duk mai son bude makarantar allo a Kano ya samar da dakunan kwanan almajirai.