- Gwamnan Kano, Abba Yusuf, ya kori dukkan jami’an da ke kula da harkokin Hajji a kananan hukumomi 44.
- Akwanakin baya ne gwamnan ya tsige babban sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano Mohammad Danbatta.
- Korar jami’an cibiyar Hajji 44 ya zo ne ‘yan sa’o’i kadan da fara jigilar alhazan jihar.
Gwamnan Kano, Abba Yusuf, ya kori jami’an da ke kula da harkokin Hajji a kananan hukumomi 44 da ke jihar,Punch ta rawaito.
Sannan Abba Gida-Gida ya maye gurbinsu da jami’an wucin gadi domin gudanar da ayyukan maniyyata aikin hajjin 2023 da ke gudana a fadin jihar.
KARANTA WANNAN: Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Farwa Kayan Al’ummah Da Sunan Ganima
Babban sakataren yada labaran sa Sanusi Dawakin-Tofa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da gwamnan ya fitar ranar Lahadi.
Gwamnan ya umurci jami’an aikin Hajji na wucin gadi da su karbi dukkan ayyuka daga tsoffin jami’an.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Ana sa ran sabbin jami’an da aka nada za su kai rahoto ga sabon Darakta Janar na hukumar a jiya (Lahadi) domin samun karin umarni a hedkwatar hukumar,” in ji sanarwar.
Idan dai ba a manta ba a kwanakin baya ne gwamnan ya tsige babban sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, Ambasada Mohammad Danbatta, ya maye gurbinsa da Alhaji Laminu Rabiu.
Korar jami’an cibiyar Hajji 44 ya zo ne ‘yan sa’o’i kadan da fara jigilar alhazan jihar.
Sama da maniyyata 700 ne daga jihar suka kasa zuwa aikin hajjin 2022 sakamakon rashin jituwar da aka samu kan zabar jirgin da zai yi jigilar maniyyata daga jihar.
A halin da ake ciki dai, a daidai lokacin da gwamnan ya sha alwashin kawar da haramtattun gine-gine da kuma tsare-tsare na Kano, da sanyin safiyar Lahadi jami’an gwamnatin jihar sun rusa wasu gine-gine a Otal din Daula da kuma sansanin Hajji.
Rushe otal din ya zo ne sa’o’i kadan bayan da jihar a ranar Asabar ta ruguza wani gini mai hawa uku, wanda ya kunshi shaguna 90 a kan titin Race Course, a unguwar Nasarawa GRA, Kano.
Lamarin da ya zama farkon rushewar gine-gine da gwamnati ta yi. wanda aka bayyana a matsayin wanda ya sabawa doka kuma an yi imanin an gina shi a filin gwamnati.
Idan dai za a iya tunawa a baya gwamnatin Dr. Abdullahi Ganduje, ya ce an gina gine-ginen da ke Otal din Daula ne bisa tsarin hadin gwiwa da jama’a masu zaman kansu.
A wani labarin kuma, Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Zulum da Buni Sun Halarci Jana’izar Tsohon Sakataren Gwamnatin Borno
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettina da wasu mashahuran mutane sun jagoranci zuwa wajen jana’izar tsohon sakataren gwamnatin Borno Usman Jidda Shuwa.
Alhaji Usman Jidda Shuwa ya rasu a ranar Asabar 3 ga watan Yuni 2023, yana da shekaru 65 a duniya.
Shuwa ya rike mukamin Sakataren gwamnati daga shekarar 2015 zuwa 2019 a lokacin Gwamna Kashim Shettima da kuma daga shekarar 2019 zuwa 2023 a karkashin Gwamna Zulum.