Gwamnatin jihar kano ta ce labarin da ke yawo a kafafen yaɗa labarai cewa ta dakatar da kwamishinan ƙananan hukumomi Alhaji Murtala Sule Garo ba gaskiya bane.
Hakan na cikin wata sanarwa da mashawarincin gwamman na musamman ka kafofin sada zumunta. Salihu Tanko Yakasai ya fitar.
Sanarwar ta ƙara dacewa wasiƙar dakatar da aikin ga kwamishinan dake yawo a kafafafen sada zumunta bata da tushi ballanta makama.
Ta cikin sanarwar wadda Salihu Tanko Yakasai yace tuni jami’an yan sanda suka fara bincike domin nemo ɓata garin dake shirin tada zaune tsaye.
Tun bayan fitowar sanarwar an yamutsa hazo dangane da labarin, inda wasu suka dinga tofa albarkacin bakinsu dangane da lamarin.