Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Ganduje ya ayyana ranar Alhamis, 20 ga watan Agusta, 2020 a matsayin ranar hutu domin murnar zagoyawar sabuwar shekarar Musulunci ta 1442 bayan hijira.
Ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da Kwamishinan yaɗa labaran jihar Muhammad Garba ya fitar a yau Laraba.
Gwamnan ya yi kira ga al’ummar Musulmin jihar da su yi amfani da lokacin wajen yin addu’o’in neman zaman lafiya da ƙaruwar arziki.
Ya kuma yi addu’ar Allah Ya kawo wa jihar ɗauki daga annobar Korona da kuma matsin da mutane suke ciki.
Sanarwar ta kuma yi kira ga jama’a da su ji tsoron Allah a cikin dukkannin al’amuransu tare da zama masu yafiya kamar yadda Musulunci ya tanadar.
Ganduje ya kuma ba da tabbacin gwamnatinsa na ci gaba da bunƙasa rayuwar al’ummar jihar.
Ana kyautata zaton cewa ranar ta Alhamis ce za ta kasance ɗaya ga watan Al-Muharram, watan farko a shekarar Musulunci ta 1442.
Laraba 19 ga watan Agusta, 2020 ita ce ta zo daidai da 29 ga watan ƙarshe na Zhul Hajji a kalandar Musulunci.