Gwamnatin jihar Legos ta yi karin bayani kan ikirarin da ta yi tun da farko cewa tana kashe kudin da ya kai Naira dubu dari 5 zuwa miliyan daya a duk rana wajen yi wa masu fama da cutar Korona wadanda ke cikin mawuyacin hali magani.
Tun da farko jaridun Nijeriya sun labarto Kwamishinan lafiya na jihar, Akin Abayomi ya bayanna a wata sanarwa cewa; Naira dubu 100 ne jihar ke kashewa wajen yi wa wadanda cutar ba ta yi mummunan tasiri a jikinsu ba magani, wadanda cutar ta kama sosai kuwa ana kashe Naira dubu dari 500 zuwa miliyan 100 kowace rana.
‘Yan Nijeriya da dama sun caccaki wannan sanarwa ta kwamishina, inda suke zargin jihar da barnata kudin al’umma, har ma wasu na kira da a yi musu cikakken bayani kan yadda ake kashe irin wadannan kudade.
Hakan ne ma ya sa a Juma’ar, nan kwamishinan yada labaran jihar Gbenga Omotosho ya fitar da wata sanarwa da zummar karin bayani, yana mai cewa an yi wa kwamishinan lafiya mummunar fahimta.
Mr Omotosho, wanda yake a taron manema labaran da kwamishinan lafiyar ya yi bayanin kudaden da ake kashewa kan masu corona ya ce, ministan lafiyar yana kokari ne ya nuna yadda ake samun yanayi na tsanani da kuma sauki a tattare da masu fama da cutar.
Omotosho ya jaddada cewa lallai gwamnatin jihar na kashe wadannan kudade a wajen yi wa masu fama da wannan cuta magani, sai dai wadanda suka yi tsanani ba su da yawa, mutane dari 2 ne kawai cikin sama da dubu 2 da ke kwance a asibiti ake kashe Naira miliyan daya duk rana wajen yi musu magani.