By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin jihar Neja ta rusa gidan wani kasurgumin mai garkuwa da mutane, wanda kwamishinan kananan hukumomi da masarautu da tsaron cikin gida na jihar, Emmanuel Umar, wanda ya jagoranci rugujewar, yace wanda ake zargin ya amsa laifin gina gidan ne da laifin daya aikata.
Gidan wanda fili ne mai dauke da daki biyu tare da karin wasu dakunan biyu da ba a kammala ba, yana cikin yankin Nkangbe a karamar hukumar Bosso ta jihar.
Umar yace matakin ya zama tinkarar wasu masu aikata laifuka da gwamnatin jihar tace ba za ta ba masu aikata laifuka damar yin amfani da jihar a matsayin maboyar su ba.Umar ya ki bayar da cikakken bayani kan ko wanene mai garkuwa da mutane da kuma yadda aka gano mazaunin na sa.
Sai dai jaridar Aminiya ta tattaro cewa ginin mallakin wani mai garkuwa da mutane ne wanda aka kama shi kuma an tabbatar da cewa ya yi amfani da wani bangare na kudaden da aka samu wajen sayen ginin.
“Wannan gini ne mallakin wani mai garkuwa da mutane da aka kama.” Wannan lamari ne na aikata laifuka kuma yana cikin manufofinmu kada mu bari wani mai laifi ya yi mulki a jihar nan.sannan “Za mu iya kafa wannan kuma daga yanzu, ba za mu bari wani mai laifi ya samu gurbi a kasarmu ba.” Yana daga cikin kudirin Gwamnan na ganin Jihar Neja ta kasance lafiya a gare mu baki daya.” Inji Umar.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Umar ya bukaci masu ruwa da tsaki a jihar dasu kai rahoton duk wani motsi da ake zargi da kuma ba da bayanai game da baki dake shigowa cikin al’ummarsu.
Kazalika “Mun gana da masu ruwa da tsaki a jihar Neja da kungiyoyin masu gidaje da masu otal da kowa da kowa kuma mun gaya musu cewa su kai rahoton duk wani motsi ko wani bako da ke shiga cikin al’umma.