Gwamnatin Saudiyya ta kori jami’anta da dama kan saɓawa ƙa’ida a kwangilar wani katafaren aikin gini da take gudanarwa na biliyoyin kuɗi.
Kamfanin dillancin labarai na ƙasar Saudiyya SPA, a ranar Juma’a ya ruwaito cewa, gwamnatin ta kuma ƙaddamar da bincike kan jami’an da ta kora waɗanda da ta ɗora wa alhakin kula da aikin.
Ana zargin jami’an da saɓa wa ƙa’ida sakamakon ba da izinin dasa gine-gine a wuraren da ba su cancanta ba wanda hakan zai iya haifar da nakasu a ingancin ginin ta yadda ba zai yi ƙarko ba.
Manyan jami’an da aka kora kamar yadda dokokin ƙasar suka tanada sun haɗar da Darakta Janar mai kula da iyakokin ƙasar da gwamnonin biranen Umluj da al-Wajh da shugabannin iyakokin biranen biyu.
https://dimokuradiyya.com.ng/babu-aikin-hajjin-bana-ga-baki-cewar-saudiyya/
Sauran jami’an da aka sallama sun haɗa da masu kula da kan iyaka a lardunan Madina, Tabuka da Assir.
Shekaru uku da suka gabata gwamnatin Saudiyya ta bayyana ƙudirin aiwatar da gina katafaren birni da zai ɗauki wuraren yawon buɗe ido da shakatawa na tarihi da kuma harkokin kasuwanci a yankin Bahar Maliya.
Yariman Saudiya, Mohammed bin Salman, shi ne ya kawo wannan tsari domin faɗaɗa hanyoyin samun kuɗi a ƙasar mai arzikin man fetur.