By Abbas Yakubu Yaura
A shirin ARC-P da aka gudanar a ranar Asabar din data gabata an yaye malamai 500 a Gombe don taimakawa wajen rage karuwar yaran da ba sa zuwa makaranta.
Shirin na ARC-P wani shiri ne na Gwamnatin Tarayya, wanda aka shirya don inganta rayuwar masu sana’a akan tituna, marayu, nakasassu, wadanda suka tsira daga auren ‘ya’ya, shaye-shayen muggan kwayoyi da kuma ‘yan gudun hijira.
Da take jawabi yayin bikin, mai baiwa shugaban kasa shawara ta musamman kan harkokin zuba jari, Maryam Uwais, ta bukaci masu gudanarwar shirin dasu taimaka wa yaran fiye da sanin ilimin da suke dashi inda ta kara da cewa ana sa ran zasu ba da horo.
Uwais ta bayyana cewa ana sa ran masu gudanarwa 500 zasu ba da rahoton yadda kowane yaro ke kula da su a kowane wata.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa aikin ARC yana da ginshikai guda bakwai da suka hada da; Ilimi da Ƙididdiga, Ƙwararrun Sana’oi da Kuɗi, kwararrun kayayyakin zamani, Ƙwararrun Rayuwa da Wasanni, Lafiya da Gina Jiki,harkar Noma da Batutuwan Yanayi, Mai gadin Ƙofa, Tsangwama da Ƙarfafawa.
“sannan ku tabbatar kun ba mu rahoton kowane wata kan yadda kowane yaro da aka ba ku ke samun ci gaba a cikin al’ummarku. Wannan babban aiki ne amma muna jin wannan ita ce hanya daya tilo da za mu iya bi wajen magance dimbin yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin kasar nan.
Yayin da take yabawa da hadin kan gwamnatin jihar Gombe wajen magance matsalolin da suka shafi yara, Uwais ta bayyana cewa jihar ta zama abin koyi ga sauran jihohi kamar Sokoto, Kaduna da jihar Borno.
A nasa bangaren, Gwamna Muhammadu Yahaya ya yabawa gwamnatin tarayya bisa wannan shiri mai nisa, inda ya kara da cewa hakan zai rage munanan dabi’u a cikin jihar.Yahaya ya tabbatar da cewa an zabo rukunin farko na masu gudanar da ayyukan a cikin jerin matasan jihar, inda ya bukace su da su zama jakadun shirin nagari.