Gwamnatin tarayya ta fitar da samarwa tare da jan hankalin ‘yan Najeriya dama kasashen duniya da su watsi da karyayyakin da IPOB ke yadawa na cewa ana kuntatawa mabiya addinin kirista a Najeriya.
Hakan ya fito ne a wata sanarwa da mai taimakawa shugaban kasa akan watsa labarai Malam Garba Shehu ya fitar, yace kungiyoyi na yada karyayyaki da kira ga kasar Amurka kan ta kawo musu dauki da irin kisan-gillar da ake musu a Najeriya.
Yace “wannan kungiyoyi basu da wata manufa da ta wuce haddasa tarzoma tsakanin Najeriya da wasu manyan kasashen duniya Kamar Amurka da Birtaniya”.
“Abun takaici shi ne wasu daga cikin wakilan wannan manyan kasashen har sun fara daukar jita-jitar, wanda wasunsu suke kafa misali da irin abina IPOB ke fada akan gallazawa kirista dake a Najeriya wanda har fadar White House ta fara yunkurin turo Malamin da zai gudanar da bincike akan lamarin”.
https://dimokuradiyya.com.ng/kanu-zai-je-majalisar-dinkin-duniya-domin-tabbatar-da-biyafara/
Shehu ya kara da cewa masu rajin kafa kasar Biafara sun dauki hayar wasu kamfanoni da zasu ke musu aikin yada karyar kuma kamfanonin suna cikin kasashe irinsu Amurka, Faransa, Birtaniya da sauransu kasashe.
Daga cikin abinda IPOB ke kokarin cimma shi ne kirkirar fadan addini a tsakanin ‘Yan Najeriya, domin su batawa Najeriya suna a idon duniya.
Idan ba a manta ba a shekarar 2017 ne gwamnatin Najeriya karkashin jagorancin Shugaba Muhammau Buhari, aka bayyana kungiyar a matsayin kungiyar ‘yan ta’adda, wanda hakan ya jawo aka kama wasu ciki har da shugabansu Nnamdi Kanu wanda ya tsere daga kasar, tare da kashe wasu daga cikinsu.