Gwamnatin tarayya a ranar Talata ta kaddamar da jami’an gudanarwa na kungiyar kifi ta Nijeriya wato NFAN, a wani mataki na samar da wani sashe da zai rika kula da kiwon kifi a Nijeriya domin cimma bukatar neman kifin da ake yi.
Edet Akpan, Sakataren ma’aikatar ma’aikatu da zuba hannun jari da kasuwanci, shi ne ya kaddamar da jami’an a Abuja a ranar Talata. Inda ya ce kaddamar da jami’an yana daya daga cikin wani mataki na gwamnatin tarayya wajen tallafawa manoma da masu ruwa da tsaki wajen bunkasa ayyukansu.
Babban Sakataren ma’aikatar ya ce hada dukkanin masu ruwa da tsaki a bangaren kiwon kifi zai bunkasa darajar kiwon kifin musamman idan suka yi aiki tare da manufa guda wajen bunkasa kiwon kifin a Nijeriya.