Wakilinmu Saleh Husain Takai
Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP sun amince zasu biya Naira dubu talatin a matsayin mafi karancin albashi a jihohin su.
Gwamnan jahar Bauchi sanata Bala Muhammad, tare da Tsohon kakakin majalisar wakilai Hon. Yakubu Dogara, suka bayyana hakan a wani taro da kugiyar gwamnonin jam’iyar ta PDP ta gudanar.
Sauran wadan da suka halarci taron kungiyar gwamnonin sun hada da, sanata Bukola Saraki, Shugaban Jam’iyar na kasa Prince Uche Secondus, tare da shugaban kwamitin amintattu na jam’iyyar Walid Jibrin.
Da ya ke yi wa manema Labaru bayani jim kadan da kammala taron kungiyar gwamnonin jam’iyar na sirri, shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Bayelsa Seriake Dickson yace, gamayyar gwamnoni PDP sun amince zasu biya naira dubu talatin a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan jahohin su.
Sai dai Dickson ya nemi gwamnatin Tarayya da ta sake duba a game da tsarin rabon Tattalin Arzikin kasar nan.
Kungiyar gwamnoni sun bukaci da a bayyana sunayen jahohin da basa bukatar abawa kananan hukumomi hakkokin su.
Gwamna Dickson yakara da cewa zaben 2019 da ya gabata ‘yar Manuniyace da PDP zata sake kama wasu guraren a zabubbuka masu zuwa.
Shugaban ya nemi shugaba Muhammadu Buhari da ya bullo da wata doka da zata hana cin zarafin Manema Labaru, da kafafen yada Labaru masu zaman kansu a kasar nan, duba da yadda suke fuskantar Barazana a lokacin da suke gudanar da aiyukan su a cikin Al’umma.