A jiya Laraba ne majalisar
zartaswa ta tarayya ta amince da kashe Naira Biliyan 58.48 don gyara hanyar nan
data taso daga Bida zuwa Saachi zuwa Nupeko da kuma gadar nan ta Nupeko zuwa
Pategi wadda ta hada jihar Neja da jihar kwara.
Ministan Ayyuka da
Ggidaje, Mista Babatunde Fashola, ya bayyana haka
ga manema labarai bayan kammala taron mako mako na majalisar
kasa
wadda mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya
jagoranta a
fadar shugaban kasa dake Abuja. Ya ce, tsohouwar kwangila ce
aka sake
farfado da ita.
Fashola, ya kuma yi nuni da cewa, ruwan sama ya nemi kawo wa
aikin
hanyar cikas, amma da yardar Allah an samu ci gaba da ayyukan
ba tare
da matsala ba.
Ministan ya kuma amince da
cewa lallai al’umma na shan wahala a wajen
zirga-zirga a wannan lokacin saboda rashin kyawun hanyoyinmu
ammma nan
gaba kadan komai zai yi daidai.