Mummunan hadarin da ya afku jiya Laraba a babbar hanyar Abaji zuwa Kwali dake Babban birnin tarayya Abuja, ya yi sanadiyar mutuwar alkalla Matasa masu yi wa kasa hidima guda biyar.
Babbar Daraktar yada labarai da Hulda da jama’a na hukumar ta NYSC, Adenike Adeyemi ta fitar da wata sanarwa Mai taken “Ranar Laraba Mai Muni ga iyalan hukumar NYSC” wato ” Black Wednesday for NYSC Family” a turan ce.
Ta ce, “Cikin jimami da bakin ciki Darakta Janar, da daukacin hukumar NYSC ke jajanta wa, iyalan matasan dake shirin fara bautan kasa, da suka rasa rayukansu a hadarin motan da ya auku, misalan karfe 2 na daren jiya, Laraba, 28 ga Yulin Shekarar 2020, a babban titin Abaji dake Kwali.” Inji sanarwar.
KARANTA WANNAN LABARIN: EFCC ta gayyaci Al-Makura da Matar shi, bisa zargin Cin hanci
“Hakazalika Dirakta Janar da daukacin hukumar na jajantawa gwamnatin jihar Akwa Ibom da na Imo, kan wannan hadarin da ya yi sanadiyar rasuwar matasan masuyiwa kasa hidima.”
A kwai Karin bayani……
A wani labarin kuma na daban
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Kasa EFCC, ta gayyaci tsohon gwamnar jihar Nasarawa Tanko Al-Makura ofishin ta dake Abuja.
Al-Makura Wanda ya yanzu yake a matsayin Sanata, hukumar ta EFFC tayyace shi ne a jiya Laraba, tare da matar shi.
A cewar wani rahoto, an gayyaci Ma’auratan ne, domin amsa wasu tambayoyi kan wani zargi da keda alaka da al’mun-da-hanan wasu kudade, lokacin da ke Gwamnan jihar Nasarawa.
Biyo bayan tambayoyin, Tsohon gwamnan ya bayyana ra’ayin shi, sabanin zargin da a ke yi mishi, inda ya ce, Hukumar EFCC ba ta taba kamashi ba, face gayyatar shi da tayi.
Al-kura ya rike mukamin gwamnan jihar Nasarawa daga shekarar 2011 zuwa 2019, inda daga bisani aka zabe shi a mastayin Sanata Mai wakiltar Yankin Nassarawa ta Kudu, a majalissar Dattijan kasar nan.
Comments 1