Hadadiyar gungiyar kwararuru masu aikin tace labaru ta kasa (NGE) tace hakkinan na nema tare da watsa labarai ba tare da wata turjiya ba na cikin wani hali a Nijeriya .
Shugaban Kungiyar na kasa , Mustapha Isah , da babban sakataren Kungiyar , Iyobosa Uwugiaren ne suka bayyana hakan a cikin wata sanarwa da suka fitar a yau yayin bikin ranar yancin yan jaridu ta duniya.
Saboda haka, sunyi kiran gaggawa domin kare kafafen yada labarai daga koma baya, inda suka bayyana cewa Dimokuradiyya zata samu koma bayane idan ana yima yancin yada labarai barazana.
Kungiyar ta NGE tayi kira ga gwamnatin tarayya da ta sauwaka farashin kayyakin da kafafen yada labarai da gidagen jaridu ke amfani dasu ,kana a saukaka haraji ga kafafen yada labarai, domin ceto su daga durkushewa.
Majalisar Dinkin Duniya dai ta ayyana 3 ga watan mayun ko wace shekara a mastayin ranar bikin yancin yan jaridu, domin fadakar da al’umma akan muhimanci baiwa kafafen yada labarai da yan jaridu yancinsu, kuma a tunatar da gwamnatoci bukatar da ke akwai na martaba yancin fadin alabarkaci baki kamar yadda sashe na 19 na kundin tsarin majalisar Dinkin duniya ya amince dashi tun a shekarar 1948.
Ranar dai ta kasaence ranar da kwararurun yan jaridu ke tattunawa akan Yancin aikin jarida da kuma ka’idojin aikin.
Taken bikin na bana shine “Aikin jarida a zamanan ce” inda ake amfani da abuwa da dama na zamani domin binciko muradun al’uma.
A wani labarin Kuma na daban.
Wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne an banka musu wuta inda suka kone kurmus a garin Kanshio da ke wajen garin Makurdi a jihar Benue.
Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu cewa, an bi su ne da sanyin safiyar ranar Litinin, inda aka kama su daura da makarantar Divine Mercy Minor Seminary da ke Kanshio inda a karshe aka kona su.
An tattaro cewa wadanda ake zargin wadanda tun farko su uku ne amma daya daga cikinsu ya tsere a lokacin da ake binsa, sun samu shiga wani gida da karfi da yaji a garin Kanshio a kokarinsu na yi wa dangi fashi bayan sun yi harbin gaggawa don kaucewa shiga tsakani.
Sai dai kuma sa’a ya ci karo da su, inda aka ce shugaban gidan ya yi ta maza inda ya kama daya daga cikinsu, lamarin da ya sa sauran mutanen biyu suka shiga tsakani da wannan jarumin har suka kubutar da abokin aikin nasu.
Wani mazaunin garin ya bayyana cewa wadanda ake zargin bayan ceto dan kungiyar nasu ne suka gudu ta hanyar tsallaka katanga inda suka hau kan babur da ke jiran su a bakin titi amma wadanda abin ya shafa suka nemin taimakon mazauna yankin lamarin da ya jawo hankalin wasu matasa da ke yankin.
Matasan dai kamar yadda aka samu sun fatattaki wadanda ake zargin har ta kai da biyu daga cikinsu suka makale a kusa da makarantar Seminary inda nan take suka banka musu wuta yayin da sauran suka tsallake rijiya da baya ta katangar makarantar suka tsere.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Benue PPRO, SP Catherine Anene, ta tabbatar da faruwar lamarin.
“An tabbatar da al’amura. Ana ci gaba da bincike, don Allah, ”in ji Anene a cikin wani sakon rubutu.