Gwamnatin Nijeriya ta ce hakurin ta ya kare kan irin hare-haren da ‘Yan Afirka ta Kudu ke kaiwa kan ‘yan kasar ta dake zama a can, inda suke kona masu shaguna da kuma sace kayayyaki.
Ministan harkokin wajen Nijeriya, Geoffrey Onyeama ne ya bayyana hakan a sakon da ya aike ta kafar Twitter inda yake cewa kasar ba za ta lamuncewa yadda wasu bata gari ke kai hari kan yan kasar ba. Wannan mataki ya biyo bayan harin da aka kaiwa ‘yan Nijeriya a karshen mako inda aka kashe uku daga cikin su, kana aka kona shagunansu a Unguwar Jeppestown dake Johannesburg.
Ko a makon jiya yayin wata Kebantacciyar ganawa tsakanin shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari da Cyril Ramaphosa na Afrika ta kudu sai da shugabannin biyu suka tabo batun hare-haren tare da lalubo hanyoyin magance su.
A lokuta da dama dai Cyril Ramaphosa na nuna damuwa da kisan ‘yan Nijeriyar a kasar sa musamman yayin ganawarsa da Buhari ko kuma da manema labarai.
A cewar shugaban ‘Yan Nijeriya mazauna kasar Afirka ta kudun, Adetola Olubajo akwai wata kungiyar bata-gari da ake kira ‘Zulu Dwellers’ ita ke da alhakin kai hare haren kan shaguna da wuraren sana’ar bakin musamman ‘yan Najeriya.
Yanzu haka dai tuni gwamnatin Nijeriya ta yi sammacin Jakadan Afrika ta Kudun a Abuja don yi mata bayani kan matakan da su ke dauka kan kisa da cin zarafin ‘yan Nijeriyar a kasarsa.