Binciken da majiyarmu ta gudanar ya nuna cewa, makarantun Sakandire na gwamnatin jihar Kaduna har yanzu ba su iya ganin sakamakon jarabawar da suka yi ba na hukumar shirya jarabawar kammala Sakandire na NECO, dalilin haka kuwa shi ne na rashin biyan kudin jarabawar da gwamnatiin jihar Kaduna ba ta yi ba na wasu dalibai da ta dauki nauyinsu.
Majiyarmu ta gano cewa, sauran makarantu masu zaman kansu dake jihar tuni dalibasu suka san abin da suka ci a jarabarwar tun da aka fitar da sakamakon a watan jiya na Agusta. Wani Malami a makarantar sakandire na Bomo a karamar hukumar sabon Gari wanda ya bukaci mu sakaya sunansa, ya bayyana cewa, kusan duk shekara sai an samu irin haka, inda gwamnatin jihar Kaduna kan dauki nauyi wasu daidaikun dalibai a makarantun gwamnati, amma sai ta yi jinkiri wajen biyan kudaden jabarawar daliban data dauki nauyin, hakan kuma ke sanya hukumar shirya jarabawar ta NECO ke rike sakamakon jarabawar makarantun da aka dauki nauyin koda dalibi daya ne kuwa gaba daya.
A kan haka ne iyaye ke kira ga gwamnati da ta gaggauta biyan NECO kudin da ta ke bin ta don a sake wa dalibai sakamakon jabawarsu, musamman ganin a halin yanzu ana hada-hadar neman gurabe a manyan makarantun kasar nan.