Harin Bwari: Sojojin Najeriya sun hallaka Ƴan ta’adda 30 da suka kai wa sojoji hari — DHQ.
Hedikwatar tsaro ta ce Dakarun Sojin Ƙasar sun kawar da 30 daga cikin ƴan ta’addan da suka kai wa sojojin na Brigade Guards hari a yankin Bwari da ke babban Birnin Tarayya Abuja ranar Lahadi.
KARANTA WANNAN LABARIN: 2023: ICPC Ta Fadada Haɗin Gwiwa Da Masu Ruwa Da Tsaki Don Magance Siyan Kuri’u
Daraktan ayyukan yada labarai na tsaro, Bernard Onyeuko ne ya bayyana haka a taron Manema Labarai na mako biyu-biyu kan ayyukan sojoji a ranar Alhamis a Abuja.
Mista Onyeuko ya ce dakarun 7 Guards Battalion da 167 Special Force Battalion ne suka gudanar da wannan samame tsakanin ranar Lahadi da Talata.
Ya ce sojojin sun yi nasarar kawar da kauyukan Kawu da Ido inda suka kawar da ‘yan ta’adda tare da lalata maboyarsu.
A cewarsa, sojojin ƙasa sun kuma kwato babura shida, bindigogi kirar AK47 guda biyu, da ƙirar LMG da dai sauran su a lokacin da ’yan ta’addan suka yi artabu.
“Shugaban Rundunar sojojin Nijeriya da sauran hukumomin tsaro na fatan sake tabbatar wa ‘yan Nijeriya jajircewarsu kan kawar da ƴan ta’adda.
“Tare da ayyukan kwanan nan da aka gudanar a tsakanin 23 ga Yuli, muna so mu tabbatar wa mazauna FCT musamman cewa ba mu da kokwanto da jajircewa a kokarinmu na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi.
“Ya kamata mutane su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullun saboda an tabbatar da tsaron lafiyarsu.
“Ana neman goyon baya da haɗin kan dukkan ƴan Najeriya saboda tsaro aikin kowa ne.
“Ana ƙarfafa ’yan ƙasa da su kai rahoton duk wani wanda ba a saba gani ba a yankuna ga Hukumomin tsaro, ” in ji shi.
A nasa bangaren, Daraktan yada labarai na tsaro, Maj.-Gen. Jimmy Akpor, ya bukaci kafafen yada labarai da su ci gaba da baiwa sojoji goyon baya wajen ganin an fatattaki makiya kasar.
A cikin sakon muryar da ake yadawa a kafafen sada zumunta na yanar gizo cewa na wani soja ne da ke da hannu a harin, Mista Akpor ya ce ba lallai ne a nemi sanin sahihancin sa ba.