An kashe akalla mutane 15 da suka hada da matan aure uku a kauyukan Binnari da Jab Jab da ke karamar hukumar Karim Lamido a jihar Taraba.
Majiyar Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ‘yan bindigar sun kai hari Binnari ne da misalin karfe 4 na safiyar yau Laraba, inda suka rika harbi ba kakkautawa.
An ce mutanen kauyen sun yi yunkurin fafatawa amma ‘yan bindigar da aka ce sun haura 50 sun yi galaba a kansu.
Majiyoyi sun shaida wa Daily Trust cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyukan biyu ne a matsayin ramuwar gayya da kashe wasu masu garkuwa da mutane da ‘yan banga suka yi a yankin makonnin da suka gabata.
An kashe ‘yan bindiga 7 a yayin arangamar kuma ‘yan bindigar da suka tsira daga harin sun tsere da gawarwakin ‘yan kungiyarsu cikin daji
A yayin harin ramuwar gayya a Jab Jab, an ce ‘yan bindigar sun kashe mutane da dama tare da kona gidaje.
Mazauna yankin da suka bukaci a sakaya sunansu, sun koka da rashin jami’an tsaro a yankin.
“Kamar yadda nake magana da ku, babu ‘yan sanda ko sojoji a Binnari amma an gaya mana cewa sojoji suna kan hanyar zuwa yankin,” in ji wani mazaunin.
Ya kuma bayyana cewa ‘yan bindiga sun kashe hakimin kauyen Binnari da wasu masu gadi a farkon wannan shekarar.
DSP Usman Abdullahi, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, ya tabbatar da faruwar harin amma ya ce an baza jami’ai tsaro a yankin..
Rahotanni na nuna cewa, Ana samun karuwar rashin tsaro a fadin kasar nan, kuma kokarin shawo kan lamarin bai haifar da da mai ido ba