Kwamishinan ‘yan sanda a babban birnin tarayya, CP Babaji Sunday, ya ce an hada hadaddiyar tawagar ‘yan sanda da sojoji zuwa Staff Quarters na Jami’ar Abuja inda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da mutane hudu a ranar Talata.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Josephine Adeh, a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce, “’yan sandan sun kuma aike da karin kayan aikin ‘yan sanda na yau da kullun zuwa manyan harabar jami’ar da tauraron dan adam domin tabbatar da tsaron mazauna yankin.
Rundunar ‘yan sandan ta ce kwamishinan ‘yan sandan ya ba da umarnin ne biyo bayan rahoton cewa wasu ‘yan ta’adda dauke da muggan makamai sun kai wa hari a Staff Quarters na Jami’ar Abuja da ke unguwar Giri a babban birnin tarayya Abuja a safiyar ranar Talata.
“Tawagar ‘yan sanda da jami’an soji na Najeriya, Bataliya ta 176 Guards, an garzaya da su cikin gaggawa zuwa yankin domin kare ‘yan kasa”.
Rundunar ‘yan sandan ta bukaci mazauna yankin da su kwantar da hankulansu, tare da yin alkawarin cewa jami’an tsaro sun yi hadin gwiwa da jama’ar yankin wajen ceto wadanda lamarin ya shafa.
Kwamishinan ya kuma tabbatar wa mazauna garin cewa za a kama wadanda suka aikata laifin tare da gurfanar da su a gaban kotu.
‘Yan sanda sun bayar da lambobin waya 08032003913, 08061581938, 07057337653 da 08028940883 a matsayin lambobin wayar da za a iya tuntubar su idan lamarin gaggawa kan tsaro.
Jami’in hulda da jama’a na Jami’ar, Dokta Habib Yakoob, wanda ya tabbatar da sace daliban, ya ce an kuma hada guiwa da jami’an tsaro domin tabbatar da tsaron ma’aikatan.