Hukumar Hisba ta jihar Kano ta cigaba da kamen matasa masu yin askin nan da bai dace ba da ake wa lakabi da kai ya ci ƙudi,
A wani rangadi da hukumar ta fito da yammacin jiya Alhamis ta shiga yankin Zooroad inda duk wanda ta haɗu da shi da askin nan da ake cewa (Kai ya ci kuɗi) za ta aske masa kai da Almakashi.
Wannan zagaye na aske kai ya fi shafar matuƙa baburan Daidaita sahu, inda za ka ga cewa wasu suna kan baɓur din ne ake tsayar da su, sannan a aske kan.
Na tuntuɓi daya daga cikin wanda aka askewa kan da ya nemi na Sakaya sunasa ya ce “To ya zan yi an tare ka anyi maka aski to ya na iya?”
Na tuntuɓi kwamandan da ke jagorantar tafiyar ya ce da Ni ba zai iya cewa komai ba kwamandan Hisba na jiha ne ke da alhakin yin magana,
Hukumar Hizba ta jihar Kano dai ta ɗade tana aiwatar da wannan aiki na aske tarin gashin da matasa ke tarawa, wanda ta ce ya saɓawa addini da al’adar mutanen Kano.