Hukumar fanshon sojoji a ranar Alhamis din nan ta ce ta biya kashi na uku na kashi 25 cikin 100 na bashin watanni 24 na karin mafi karancin albashi na kasa ga wadanda suka cancanta.
Shugaban hukumar Rear Adm. Saburi Lawal, a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, ya ce an biya kudin ne a ranar Alhamis din nan.
Lawal ya ce kashi na uku an biya ne ga wadanda suka cancanci aikin soja da ke aiki da asusun hukumar.
Ya kuma kara da cewa, hakan na kuma cika yarjejeniyar da hukumar ta cimma da ma’aikatar kudi, kasafin da tsare-tsare ta kasa (FMoFBNP) na fitar da kudaden da aka ware a duk shekara.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Shugaban ya ce an biya dukkan ‘yan uwa da suka rasu na ‘yan fanshon soja, wadanda ke da hakki.
Ya shawarci duk masu karbar fansho na soja da abin ya shafa da su tuntubi bankunan su domin samun hakkin na su.
KARANTA WANNAN: https://dimokuradiyya.com.ng/buhari-ya-karbi-bakuncin-tinubu-da-shattima-a-gidan-gwamnati/
“A madadin mu masu karbar fansho na soja, hukumar na mika godiya ga shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa gagarumin goyon bayan da yake baiwa hukumar da sojoji masu ritaya.
“Har ila yau, hukumar ta mika godiyarta ga Ministan Tsaro, Manjo Janar Bashir Magashi mai ritaya, da babban hafsan hafsoshin tsaro, janaral Lucky Irabor da kuma hafsoshin tsaro bisa goyon bayan da suke ba su a kai-a kai domin cimma buri da kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.
“Har ila yau, hukumar za ta so gode wa manyan sojojin mu da suka yi ritaya saboda hakuri, fahimta da kuma ci gaba da goyon baya,” in ji shi.
Lawal ya yi alkawarin tabbatar da biyan kashi na hudu kuma na karshe na bashin kafin karshen shekarar nan.
(NAN)