Hukumar sasantawa kan Gaskiya a Gambia a ranar Juma’a ya ba da shawarar a gurfanar da tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh a gaban kotun kasa da kasa kan laifukan da ake zarginsa da aikatawa a lokacin mulkin da yayi na kama karya na shekaru 22.
Hukumar ta ba da shawarar ” gurfanar da Yahya Jammeh da wadanda ke da hannu a cikin wata kotun kasa da kasa a yammacin Afirka a wajen kasar Gambia, karkashin inuwar kungiyar Tarayyar Afirka ko kuma kungiyar ECOWAS,” in ji sanarwar.
“A cikin shekaru 22, tun daga ranar 22 ga Yuli, 1994, Yahya Jammeh da abokan aikata laifin sun aiko babban laifi ga al’ummar kasar Gambia,” in ji sanarwar.
A watan Janairun 2017 ne Shugaba Adama Barrow ya kafa hukumar ta gaskiya da sasantawa, wanda zabensa a shekarar 2016 ya kawo karshen mulkin kama-karya na sama da shekaru ashirin.
Hukumar wadda ta saurari shaidu kusan 400, ta gabatar da sakamakon binciken ga Barrow a ranar 25 ga watan Nuwamba, inda ta bukaci gwamnati da ta cigaba da tuhumar sa da aikata laifuka, amma ba a bayyana rahoton ko sunayen jami’an da ta ce da laifi ba har sai ranar Juma’a.
Jammeh ya kwace mulki a shekarar 1994, kuma ya shafe shekaru 22 yana kula da gwamnatin da ake zargi da aikata muggan laifuka kamar kisan kai da azabtarwa da fyade da gwamnatin kasar ta amince da shi.
Ya tafi gudun hijira a Equatorial Guinea a cikin 2017 bayan nasarar Barrow a zaben amma yana da babban goyon baya a kasar.
AFP