Hukumar Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta jihar Kano ta dakatar da dukkan jarrabawar da aka shirya gudanarwa tun daga ranar 8-11 na safiyar Litinin 10 ga watan Janairun 2022.
Solacebase ta ruwaito cewa jami’ar ta sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadin ta hannun shugaban kwamitin jarrabawar jami’ar, Dakta Ya’u Datti a ranar Lahadin.
Sanarwar ta ce dakatar da jarrabawar a wadannan lokutan ya biyo bayan shawarar da masu tuka babur mai suna “Adaidata Sahu” suka yi.
“Daga baya kwamitin jarrabawar jami’ar zai tuntubi mataimakin shugaban jami’ar domin yanke hukunci kan makomar sauran jarrabawar da aka yi a ranar,” in ji sanarwar.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa masu tuka babur tun ranar Juma’a suna raba takardu tare da sanarwar yajin aikin ga mambobinta.
Wannan lamari dai ya samo asali ne kan matsalolin da ba a warware ba tsakanin masu tuka keken Adaidaita sahun da hukumar KAROTA.
Comments 1