Babban Daraktan hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano (KAROTA), Baffa Babba DanAgundi, ya kori daya daga cikin jami’an hukumar, Jamilu Gambo.
An kori Gambo ne biyo bayan rashin da’a a wajen aikinsa inda aka ce ya lalata tayar Babban motar bayan takaddama tsakaninsa da direban Babban Motan.
Sauran direbobin tirela sun tare hanyar Kano zuwa Hadejia domin nuna goyon bayansu ga abokin aikinsu, lamarin da ya janyo wa matafiya da sauran direbobin da ke kan hanyar suka wahala.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar Nabulusi Abubakar Kofar Naisa, a wata sanarwa da ya fitar, ya nemi afuwar jama’ar da kuma samu jinkirin daukar matakin Hukumar, sakamakon faruwar lamarin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Na Himmatu Wurin cigaba da Kawo Kuduri Masu Tasiri Ga Nigeria
Ya ce an mika jami’in da aka kora ga rundunar ‘yan sanda domin ci gaba da bincike tare da biya diyya direban Motar da akayi wa banna.
A wani labarin Kuma na daban.
Wani mai suna Reprieve yazo da wata yarinya mai shekaru 16 mai suna Joy Abahi Amuh wadda ta samu mafi kyawun sakamakon jarabawar WAEC a shekarar 2020 a jihar Benue a matsayin wata kungiya mai zaman kanta data ba ta Naira 500,000 don samun damar ci gaba da karatun ta.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Joy ta sami makin “A” a duk darussa tara da ta rubuta a makarantar sakandare ta St Paul, Otukpo a Jarabawa WAEC.
Sai dai kuma rashin kudi ya hana ta yin jarrabawar shiga manyan makarantun gaba da sakandare (UTME) na shekarar 2021, hakan ya sa ta dauki matakin koyarwa a makarantar firamare Reno domin ta samu damar ajiye kudi da zata ci gaba da karatun ta.
A yayin da take koyarwa, ta zo ne kwanaki kadan da wata kungiya mai zaman kanta ta (ESLF), tare da hadin gwiwar (BIPC), inda ta ba ta kyautar tsabar kudi Naira 500,000 a matsayin ” Mafi kyawun Dalibi ”a cikin jihar a 2020.
Manajan Darakta na BIPC, Barista Alex Adum, ya ce kyautar ta dace da kuma cancanta don taimakawa wajen neman ilimi.
Sannan ya ce, “Mun zabi gudanar da wannan karramawar ne domin karfafa ƙwazo a fannin koyo da aiki tuƙuru a tsakanin matasanmu masu tasowa.
Kazalika Joy wacce ta fito daga unguwar Igaluwa dake gundumar Ugboju a karamar hukumar Otukpo ta jihar, ta halarci makarantar firamare ta RCM, Ipom-Ugboju, sannan ta wuce makarantar sakandare ta St Paul, Otukpo.
Shugaban makarantar St Paul, Mista Peter Emaikwu ya ce Joy daliba ce mai kwazo da mai da hankali akan karatunta.