Hukumar Kasar Dubai sun haramta zirga-zirgar Jirage daga Najeriya
Kasar ta Dubai ta dakatar da shige da fice na Jirage har sai bayan awa 48.
Sai dai a ranar Lahadi data gabata ne Hukumar Dubai ta Kara zangon dakar data saka.
KARANTA:- Jam’iyyar APC reshen Jahar Filato na shirin fidda gwani
Tace watanni masu yawa nanga Koda Jirage daga Najeriya zasu shiga saboda cutar Covid-19.
Hukumar ta sanar da tsari na adadin mutane daga kasar Najeriya, Italiya da indiya da zasu rinka shiga kasar.
Sun ce Mutane daga Najeriya sai sun gabatar da takardar shaidan gwaji na kasa da awa 48 kamin tashin Jirgi.
Sun ce dole takardar kowane mutun ta kasance tana dauke da lambobin sirri, kuma dole takardar tazama tafito daga wani Asibiti da gwamantin Najeriya ta amince dashi.
Daga karshen dai kasar Dubai din tace zirga-zirgan Jirage zai cigaba daga 23 ga watan Yuni.
Ta Kara da cewa dole mutumin da zai fito daga Najeriya ya kasance kwana sha hudu baya kamin tafiyar Yana Kasar.
Tace kasar zata cigaba ta shiryawa wajan tarbar mutane daga kasar Najeriya.