Hukumar hana fasa ƙwauri ta ƙasa, Kwastam na shirin samar da kudi Naira tiriliyan 2 a bana kuma ana sa ran za a samar da kusan N1.6tn na wannan kudi daga shiyyar Kudu maso Yamma.
Wani rahoto daga hukumar ya ce hukumar na samar da kusan kashi 80 cikin 100 na kudaden shigar da take samu a duk shekara daga jihohin Legas da Ogun da Ondo da kuma Oyo.
DUBA WANNAN LABARIN: Zaben Anambra: Dillalan Man Fetur zasu dakatar da kasuwancin su a yau
Bayanan da aka samu daga bangaren jiragen ruwa da tashoshin jiragen ruwa suka samu daga hukumar kwastam sun bayyana cewa jihohin Kudu-maso-Yamma guda hudu ne ke da kashi 80.48 na kudaden shiga na hukumar Kwastam ɗin.
Rahoton ya ci gaba da cewa, “Bayanan sun kara nuna cewa daga cikin kudaden shigar Naira tiriliyan 2 da hukumar ke sa ran za a samu a bana, ana sa ran za a samu Naira tiriliyan 1.61 a Kudu maso Yamma, naira biliyan 264.2 daga Kudu maso Kudu, sannan Naira biliyan 36.53 daga Kudu maso Kudu.
“Hukumar NCS kuma tana sa ran samar da Naira biliyan 35.35 a Arewa maso Yamma, da Naira biliyan 20.21 a Arewa ta Tsakiya, da kuma Naira miliyan 662 daga Arewa maso Gabas.” kamar yadda rahoton ya bayyana.
Comments 1