Hukumar lafiya ta duniya (WHO) tana sa ran yi wa yara aƙalla miliyan ɗaya da dubu ɗari ɗaya allurar rigakafin zazzaɓin cizon sauro domin kare su daga cutar a bana.
Babbar jami’ar hukumar a Najeriya kan kula da zazzaɓin na malariya, Misis Iniabasi Nglass ta bayyana hakan yayin ƙaddamar da gangamin yaƙi da cutar a sansanin ‘yan gudun hijira na El-Miskin da ke Maiduguri.
Ta ce an shirya gangamin ne don ganin a bana cutar ba ta yi tasirin da ta saba yi a lokacin damina ba.
“Yayin gangaminmu na ƙarshe a watan Yuli, mun yi wa yara miliyan ɗaya da dubu ɗari ɗaya rigakafin, kuma yawancinsu ‘yan shekara uku zuwa watanni 59 da haihuwa ne daga ƙananan hukumomi 25 na Jihar Borno,” inji Misis Iniabasi.
Babbar jami’ar ta ƙara da cewa shirin zai gudana ne sau huɗu a cikin kwanakin marka-marka na daminar bana wanda a cikinsu ne aka fi samun ɓarkewar zazzaɓin.
https://dimokuradiyya.com.ng/zuwa-2050-za-a-kawo-karshen-cutar-maleriya-who/
Ta ce rigakafin ta kan yi aiki na tsawon kwanaki 35 a jikin yaran da aka yi wa.
Yayin rigakafin watan Yuli, babbar jami’ar ta ce sun samu nasara 100 bisa 100 saboda haɗin kan da iyayen yara suka ba su.
Shi kuwa babban jami’in shirin yaƙi da zazzaɓin cizon sauron a jihar, Mala Waziri, cewa ya yi a shekarar 2017, ƙananan hukumomi 12 ne kacal suka ci gajiyar shirin, saɓanin bana da 25 suka amfana.
Ya ce ƙananan hukumomin Marte da Abadam ne kawai gangamin bai sami damar zuwa ba saboda matsalar tsaro.
Ya kuma yi gargaɗin cewa yaran da suke zaune a sansanonin ‘yan gudun hijira sun fi fuskantar barazanar kamuwa da cutar saboda sauron da ya ke cizon su.