Hukumar kula da kayayyakin more rayuwa ta kimiyya da injiniya ta kasa (NASENI) ta ce za ta horar da matasa 100 a Kebbi kan dabarun noman zamani.
Dr Muhammad Muhammad, Daraktan sayan kayayyaki na hukumar a jihar ne ya sanar da haka a wata ziyarar ban girma da ya kai wata kungiya mai zaman kanta, ta Khadimiyya for Justice and Development Initiative, a Birnin Kebbi ranar Asabar din nan.
Ya ce, “Za mu shirya wani horo na kwanaki biyar ga matasa 100, wadanda aka zabo daga kananan hukumomi 21 a kan hanyoyin noman zamani, ta hanyar amfani da ingantattun kayan aikin noma.
“Hukumar ta kammala dukkan shirye-shiryen kafa cibiyar horarwa a jihar”.
Ya godewa wanda ya kafa kungiyar mai zaman kanta, Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, da ya kafa ta domin taimakawa al’ummarsa.
KARANTA WANNAN: https://dimokuradiyya.com.ng/ba-mu-tafi-yajin-aiki-ba-barazana-daga-bangaren-kudu-maso-gabas-ne-ipman/
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Muhammad ya kuma bayyana Malami a matsayin “mai taimakon jama’a wanda a kullum zuciyarsa ke taimakon mabukata”, ya kuma bukaci sauran masu hannu da shuni da su yi koyi daga shi.
Ya yabawa Khadimiyya bisa bayar da gudummawar fili mai fadin hekta 20 a garin Bagudu domin gina cibiyar koyon sana’o’i a karamar hukumar Bagudu.
“Cibiyar ta kwantar da hankalin al’umma da al’ummar jihar. Za a yi amfani da shi wajen hada kai da kuma baiwa matasa horo a kananan hukumomi da jiha da Najeriya baki daya,” inji shi.
Muhammad ya kuma yabawa wannan kungiya mai zaman kanta bisa kasancewarta tagari abokan aiki tare da yin taka tsan-tsan wajen tantance wadanda za a horas da su a fadin jihar.
Shugaban Sakatariyar NGO kuma Sakataren Yada Labarai na kasa, Alhaji Ibrahim Abubakar-Jombali, ya godewa hukumar bisa sabon alkawarin da ta dauka na ciyar da aikin noma na zamani gaba a jihar.
Ya yabawa irin jajircewa da cikakken goyon baya da hadin kai da Khadimiyya ta ba hukumar domin ganin ta cika aikinta.
“Hadin gwiwar da ke tsakanin kungiyoyi masu zaman kansu da hukumar za ta kawo manufofin da ake so na ciyar da harkar noma gaba a jihar.
“Khadimiyya kungiya ce mai zaman kanta da Malami ya kafa, da nufin rage radadin talauci da samun adalci ga talakawa.
“Ya zuwa yanzu, ta gina rijiyoyin burtsatse sama da 300 a fadin jihar, sannan ta samar da ayyukan yi ga matasa sama da 700 da ba su da aikin yi, ta raba kudaden tallafi don rage radadin cutar COVID-19, sannan ta raba sama da fom din JAMB 5,000 ga dalibai marasa galihu.
“Har ila yau, ta ba da gudummawar motoci ga Hukumar Kula da Lafiya ta Jihar Kebbi (KECHEMA), Cibiyar Islama ta Abdulahi Fodio, Dakarun Al’adun Kebbi, da sauran kungiyoyi tare da bayar da tallafin kudi ga zawarawa da marayu a dukkan sassan siyasar jihar 225.” Yace.
Abubakar- Jombali ya kara da cewa ayyukan jin kai na kungiyar ya zarce jihar ne ta hanyar bayar da tallafin kudi na Naira miliyan 5 ga wadanda bala’in gobara ya shafa a kasuwannin Katsina da Gusau ta tsakiya, jihohin Katsina da Zamfara, bi da bi.
“Mun ba da gudummawar kayan aikin jinya ga asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello (ABUTH) da ke Zariya, Jihar Kaduna da Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya Jalingo, Jihar Taraba, da dai sauransu,” inji shi.
(NAN)