By Abbas Yakubu Yaura
A ranar Talata Najeriya ta sami sabbin mutane 159 wadanda suka kamu da cutar COVID-19 a cikin jihohi 13 ciki harda da birnin tarayyar FCT.
Cibiyar hana yaduwar cututtuka ta Najeriya itace ta bayyana hakan a shafinta na yanar gizo da safiyar Laraba.
Cibiyar ta kuma ce ba a sami rahoton mutuwar mai alaka da cutar COVID-19 ba.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa, karin wadanda aka samu na Mutane 159 a ranar Talata sun nuna an samu raguwar masu dauke da ita acikin mutane 711 da aka samu a kasar a baya.
Cibiyar ta ce FCT da Legas sun sami adadin mafi yawan masu kamuwa da cutar inda dukkansu suka ba da rahoton bullar cutar guda 28 kowanne, sai Nasarawa guda 25, Fulato 24, Kwara 22, da Delta takwas, Kano takwas, Rivers bakwai,sai Edo guda biyu. Bauchi ma guda biyu, Bayelsa – biyu, Kaduna guda daya, Sokoto daya da kuma Taraba itama daya.
Hukumar ta ce sabbin cututtukan COVID-159 sun kawo adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a kasar zuwa 211,330.
Kazalika, ta kara da cewa majinyata 202,803 na cutar COVID-19 sun murmure kuma an sallame su a cikin kasar.
Inda ya kara da cewa Cibiyar Bayar da Agajin Gaggawa ta kasa mai sassa daban-daban, wacce aka kunna a matakin II, ta ci gaba da daidaita ayyukan mayar da martani na kasa.
NCDC ta ce sama da mutane miliyan 3,298,966 ne aka yi wa gwaji daga kusan mutane miliyan 200 na kasar.