By Abbas Yakubu Yaura
Hukumar samar da ayyukanyi ta kasa (NDE), a jihar Nasarawa, tace ta fara horar da mutane 540 shirin (ABT) da kuma fadada Ayyukan jama’a na musamman (ESPW- 774, 000) don basu damar dogaro da kai da bada gudummawar su ga ci gaban kasa.
Shugaban gudanarwar hukumar na jihar Mista Chris Bamsida ne ya bayyana haka a ranar Larabar yayin wani taron horar da ‘yan kasuwa na kwana biyu (ABT) ga mahalarta taron a Lafia, Akwanga da Keffi.
Sannan yace horon na da nufin tasiri ga mahalarta taron tare da kwararrun sana’o’in hannu domin ci gaban kasa baki daya.“Wannan taron yana da nufin yin tasiri ga ci gaban dabarun kasuwanci a cikin ku don baku damar fahimtar ƙalubalen zamani na kasuwanci da gudanar da kasuwancin ku yadda ya kamata.
“A bisa wannan ra’ayi, an zabo masu cin gajiyar shirin 180 daga kowadanne gundumomin sanatoci uku na jihar, kuma ana sa ran za a horas da masu cin gajiyar 540 a jihar,” inji shi.
Bamsida yace a yayin horon, za a wayar da kan mahalarta taron kan karfafa gwiwar kasuwanci, dabarun talla, yadda ake samar da ra’ayoyin kasuwanci, rubuta nazarin yiwuwar samun kudade daga hukumomin kudi da dai sauransu.sannan yace ya yabawa gwamnatin jiha bisa samar da yanayi mai kyau ga NDE don cimma burinta a jihar.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa yi kira ga gwamnatin jihar da daidaikun jama’a da kungiyoyi masu zaman kansu dasu tallafa wa wadanda suka amfana domin rage zaman kashe wando da talauci a jihar.
Kazalika Da yake mayar da martani, wanda ya ci gajiyar shirin, wanda ya yi magana a madadin sauran wadanda suka ci gajiyar shirin, Mista Ewuga Anzari, ya yaba wa hukumar bisa wannan horon da take bayarwa tare da alkawarin zama jakadan nagari a shirin.