Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa reshen jihar Kano ta kama wata babbar mota da ake zargin ta shigo da miyagun ƙwayoyi jihar.
Shugaban hukumar ta ƙasa shiyyar Kano Dr Ibrahim Abdul ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai a hedikwatar hukumar dake Kano.
https://dimokuradiyya.com.ng/hukumar-ndlea-ta-damke-wata-mota-shakare-da-tabar-wiwi-a-jihar-kano/
Dr. Ibrahim Abdul ya ce, dama sun samu rahoton sirri game da shigowar motar hakan ya sa suka yi shiri na musamman, inda suka bi bayan ta tun daga titin Zaria.
Ya ƙara da cewa, a binciken da suka gudanar sun gano motar ta ɗauko magunguna ne amma sai aka cakuɗa su da miyagun ƙwayoyi.