By Abbas Yakubu Yaura
Hukumar tsaro ta farin kaya ta Najeriya,NSCDC, ta tabbatar da cafke wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne su uku wadanda suka tsere daga unguwar Magami a jihar Zamfara, sakamakon yadda jami’an tsaro suka takurasu.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar ta NSCDC, Mista Ikor Oche, ya tabbatar da faruwar lamarin a wani taron manema labarai, inda yace an kama wadanda ake zargin ne a wurin shakatawa na manyan motoci na jihar da ke Gusau ranar Litinin.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa an kama wadanda ake zargin ne da sanyin safiya yayin da suke kokarin shiga wata mota da za ta nufi Taraba domin shiga cikin sauran mambobin da suka koma.
Sannan ya ce, “Tukur Halilu, mai shekara 27, ya fito ne daga kauyen Gabaru, dake gundumar Nuhuche, a karamar hukumar Bugudu ta jihar, kuma wanda yake a karkashin wani fitaccen shugaban ‘yan bindiga, Magajin Kaura.”
A cewarsa, Halilu ya tabbatar da cewa yana yin satar shanu a dukkan kauyukan dake kusa da karamar hukumar.
Baya da haka ya ce wasu mutum biyu da ake zargi, Mista Hussaini Altine, mai shekaru 40, da Mista Abubakar Altine mai shekaru 60, sun fito ne daga kauyen Agamafiya, unguwar Rijiya, dake karamar hukumar Gusau.
“Duk da cewa Abubakar Altine ya yi ikirarin cewa ba shi da laifi, Hussaini ya amsa cewa shi yana cikin sansanin ‘yan ta’addar Gugurawa,” in ji shi.
Kakakin hukumar NSCDC, yace Hussaini Altine ya shiga cikin hare-haren ‘yan ta’adda guda uku a Kurya, Bagawuri, Agamalafiya da Rijiya.
Ya kara da cewa kama wadanda ake zargin zai taimaka wajen gudanar da bincike mai zurfi wanda zai iya haifar da kama wasu da ake tuhuma kafin a gurfanar da su gaban kuliya.