Wakilinmu Mu’azzam Yakubu Sanka
Hukumar yaki da al’mundahana da karban koken jama’a ta jihar Kano zata kirkiro da wata hanyar hada kai da Shuwagabannin addinai domin wayar da kan jama’a wajen goyon bayan yaki da rashin gaskiya a jihar.
Shugaban Hukumar Barr. Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana haka yayin da ya karbi Bakuncin Shuwagabannin kungiyar hadakar addinai mai rajin yaki da al’mundahana a ofishin sa da ke jihar Kano.
Rimin Gado, yace Kungiyar tana da muhimmiyar rawar da zata taka wajen fadakar da jama’a da cusa masu kyamatar rashin gaskiya a zukatan su, da kuma koyar da su hanyoyin da zasu yake ta.
Don haka ne yace akwai bukatar samun hadin kan kungiyar ta hanyar samar da takardar fahimtar juna da ake kira MOU a turance
Barista Muhuyi, ya kara da cewa hukumar tana kan tallafawa hukumomi da dai-daikun jama’a wadanda mafi yawa ta karbo Musu dukuyoyin su da aka so ayi sama da fadi da su bila adadin a jihar kano.
Tunda farko a nashi jawabin shugaban Kungiyar, Bishop John Niyiring, yace sun kawo ziyarar ce domin gabatar da kawunan su ga hukumar da kuma nuna mata niyar kungiyar na goyon bayan ta a duk abin da ta sa gaba.
Ita dai kungiyar ta kunshi manyan masana addinan Islama da kiristanci, domin kawo cigaba Mai Ma’ana a Kasar nan.
Usman Bello,
Daraktan kula da ayyuka na musamman.