Babban Sifeton ‘yan sandan Najeriya, Muhammed Adamu ya haramta duk wani gangami na mabiya akidar Shi’a karkashin Sheik Ibrahim El-Zakzaky da ke tsare a hannun hukumomin kasar nan.
Adamu ya kuma bayyana cewa, rundunar ‘yan sandan kasar za ta dauki duk wani mamban kungiyar ta ‘yan Shi’a a matsayin dan ta’adda, sannan kuma za ta dauki mataki kamar yadda dokar ta’addanci ta 2013 ta bada dama.
Babban Sifeton ya bayyana haka ne a ranar Talata a yayin bude taron manyan jami’an ‘yan sandan kasar da suka saba gudanarwa a duk karshen wata a Shalkwatansu da ke birnin Abuja.
A ranar 26 ga watan Yuli ne, wata babbar kotun tarayya ta ce, gwamnatin Najeriya ta ayyana kungiyar Islamic Movement of Nigeria a matsayin ta ‘yan ta’adda, yayinda ta haramta ayyukan kungiyar karkashin jagorancin El-Zakzaky.