Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasar nan, Yan bindiga bazasu Kara samun maboya ba.
Yayin da yake jawabi ga wakilan jam’iyyar PDP a Katsina a ranar Laraba, Atiku ya ce sakacin shugabanni ne ya ba masu laifi damai ci gaba danumfashi.
Ya ce idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben shekarar 2023 zai tabbatar da cewa babu wani mai laifi da zai tayar da ta’addanci a kan ‘yan kasa da ba su ji ba ba su gani ba kuma masu son zaman lafiya ba tare da komowa ba.
“Muna tahowa Katsina tare da tsohon gwamnanku Ibrahim Shema a cikin jirgi na na kashin Kai, kuma babu inda ba mu iya gani a kasa. Ina abin da ake cewa dajin da masu laifi suke boye da ba za a kai gare su ba?.
“Ina tabbatar muku da cewa idan kuka ba ni goyon bayanku na zama shugaban kasa a 2023, batun rashin tsaro zai kasance cikin manyan abubuwan da muka sa a gaba, kuma na yi alkawarin dawo da zaman lafiya a Katsina da kasa baki daya.
Daga nan Atiku ya bayyana sauran bangarorin da zai mayar da hankali a kai idan aka ba shi dama, da suka hada da hadin kan kasa, tattalin arziki, ilimi, da mika mulki ga jihohi.
Ya godewa wakilan Katsina bisa abin da ya kira goyon bayansu a shekarar 2019 a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas, inda ya ce sun taimaka masa wajen ganin ya zarce sauran masu son daga tutar jam’iyyar.
A cikin tawagarsa akwai Cif Raymond Dokpesi da Sanata Baraka Sani da Sanata Abdul Ningi da Alhaji Adamu Maina Waziri da tsohon sakataren PDP na kasa Umar Tsauni.