Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Tinubu, ya bayyana mamakinsa cewa jam’iyyar PDP har yanzu tana nan a matsayin jam’iyyar siyasa.
Ya ce duba da yadda jam’iyyar ta kasance a cikin shekaru 16 da ta yi tana mulkin kasar nan, bai iya ganin hanyoyin jiragen kasa da za su iya yin jigilar mutane da dabbobi, da jigilar abinci daga Kudu maso Yamma zuwa Arewa ba.
KARANTA WANNAN LABARIN: Limami Ya Mutu A Hanyarsa Ta Dawowa Daga Jana’iza
Dan takarar shugaban kasar yana magana ne a wajen kaddamar da tambarin Tinubu/Shettima 2023, ranar Asabar a Abuja.
Ya ce yayin da jam’iyyar PDP ke ci gaba da fafutukar neman shugabancin jam’iyyarsu tana neman alkiblar makoma.
Ya ce, “Ina mamakin dalilin da ya sa PDP ta wanzu a matsayin jam’iyya, inda ba ta iya ganin kayayyakin aikin jirgin kasa da za su iya yin jigilar kayayyaki, mutane da dabbobi, da jigilar abinci tun daga fadin kasar nan ba, alhalin ina amfani da layin dogo. mu je Arewa, muje Kano daga Legas idan muna hutu. Sun isa can suka mayar da shi injin kyankyasar kajin.”
A wani labarin kuma, A Kwai Kimanin Sama Da Bindigogi Miliyan 6 A Hannun Fararen Hula – Rahoto
Akalla a kwai kimanin bindigogi sama da miliyan 6,154,000 da ke hannun fararen hula a Najeriya, kamar yadda rahoton da SBM Intelligence ya fitar.
Makaman dai a cewar rahoton sun kai kashi 3.21 cikin mutum 100, yayin da jimillar bindigogi dubu 224,200 da dubu 362,400 ke hannun dokar soji da sauran jami’an tsaro, bi da bi.