Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce gwamnatinsa ta dukufa wajen ganin an farfado da ababen more rayuwa ga yan Najeriya sakamakon yadda ci gaban kasar ya dogara ga bangaren.
Shugaban ya bayyana hakan ne a yau Alhamis yayin wata ganawa da shugaban bankin ci gaban Musulunci (IDB), Dr Mohammed Al-Jasser, a wani bangare na taron zaman lafiya dake gudana a birnin Paris na kasar Faransa.
A cewar wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Mista Femi Adesina ya fitar, Buhari ya kuma yi nuni da cewa ‘yan Najeriya za su iya kula da kansu idan aka samar da duk wasu kayayyakin more rayuwa a kasar.
Shugaban ya godewa hukumar gudanarwar bankin bisa taimakon da suke bayarwa kawo yanzu, yana mai cewa “abin da muka dogara da shi (danyen mai) kuma cike yake da kalubale, domin kuwa Yana dawowa a hankali, kuma muna ƙara samun kwarin gwiwa duk da hakan. Amma muna sa ran babban hadin kai daga gare ku.”