Kasar Iran ta ce ta dakile wani yunkurin da sojojin ruwan Amurka suka yi na kwace wani jirgin dakon mai a tekun Oman dauke da mai, kamar yadda gidan talabijin din kasar ya ruwaito.
To sai dai Iran ba ta bayar da cikakken bayani kan ranar da lamarin ya faru ko kuma kasar da ke da rajistar jirgin a cikin rahoton, wanda ke zuwa a daidai lokacin da ake kokarin farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran da manyan kasashen duniya da za ta sa a janye takunkumin da Amurka ta kakaba mata na fitar da mai.
Kamfanin dillancin labaran IRNA ya rawaito cewa, sojojin Amurka sun bi jirgin dakon mai da jirage masu saukar ungulu da jiragen yaki amma sun kasa kama shi, inda ya kara da cewa yanzu haka jirgin yana cikin yankin ruwan Iran.
DUBA WANNAN LABARIN: Yanayin da ake ciki kan kwararar Iskar Gas a Ikeja
Tashar talabijin ta Iran a ranar Laraba ta bayyana lamarin a matsayin yunkurin “satar” mai da bai yi nasara ba. Haka kuma ya gaza bayyana lokacin da lamarin ya faru.
Wannan ci gaban ya zo ne gabanin tattaunawar nukiliyar da aka shirya gudanarwa a karshen wannan watan.
Comments 2