Babban jigon zanga-zangar kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar Najeriya Omoyele Sowere ya bayyana a shafinsa na Twitter cewa, jami’an tsaro sun fito suna ƙoƙarin muzguna wa wasu masu zanga-zangar a Legas.
A wani sako na daban da shi ma ya wallafa a shafinsa na Twitter, Deji Adeyanju wanda jigo ne, game da zanga-zangar, ya bayyana cewa an kama aƙalla masu zanga-zangar su 60 a birnin Abuja.
Hotunan yadda jami’an tsaro suka dinga kama masu Zanga-zangar ya shafe kafafen sada zumunta tun a jiya Laraba da safe har zuwa yanzu, kuma mutane da dama na tofa albarkacin bakinsu dangane da lamarin.
Masu zanga-zangar sun ce sun fito ne domin umartar gwamnati da ta gyara yadda take gudanar da harkokinta.
Sai dai har yanzu ba a ji daga bakin gwamnatin tarayya ba dangane da lamarin da kuma irin matakim da zata ɗauka.