Jami’an ‘yan sanda a jihar Katsina sun kashe ’yan ta’addan da ake zargin kai hare-hare a ƙaramar hukumar Batsari.
Kakakin hukumar SP Gambo Isa ne ya shaida wa manema labarai, cewa rundunar ta samu nasarar ne bayan wani farmaki da mahara kusan 40 suka kai a ƙauyen Zamfarawa a karamar hukumar a ranar 6 ga watan Agusta.
Ya ce ’yan bindagar sun kashe dattawa biyu da suka haɗa da Yakubu Idris mai shekaru 70 da kuma Shafi’u Suleiman mai shekaru 65, sannan suka yi awon gaba da dabbobi masu yawa.
Bayan samun rahoton harin ne ’yan sanda suka bi sawun ‘yan bindiga da suka shige cikin jeji inda suka yi musayar wuta da su.
https://dimokuradiyya.com.ng/yan-bindiga-sun-hallaka-mutum-33-a-zangon-katat-na-jihar-kaduna/
Ya ce ’yan sandan sun kashe mutum ɗaya nan take yayin da saura da suka samu raunuka suka sha da ƙyar a cikin dajin.
Washegari rundunar ta je ƙauyen Barankada bayan samun rahoto, inda ta tsinci gawarwakin mutum 7 daga cikin waɗanda aka harba suka shiga daji da raunukan.
Rundunar ta kuma gano wasu layu da ‘yan bindigar ke amfani da kuɗi Naira dubu ashirin da ’yan kai da kuma alburusai da wasu kaya da aka samu.