Awanni kaɗan bayan ‘yan Majalisar dokokin jihar Edo sun tsige mataimakin kakakin majalisar Hon. Yekini Idiaye, jami’an ‘yan sanda sun mamaye harabar majalisar.
‘Yan sandan sun ce sun ɗauki matakin ne don kaucewa abinda ka iya zuwa ya dawo sakamakon tsige kakakin majalisar.
An dai tsige Idiaye ne a ranar Laraba yayin zaman majalisar a birnin Benin.
An dai tsige ɗan majalisar ne wanda shi ne yake wakiltar mazabar Akoko-Edo ta ɗaya tare da wasu takwarorinsa su huɗu a majalisar saboda nuna goyon bayansu ga ɗan takarar gwamnan jihar a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar APC, Osagie Ize-Iyamu.
Sauran ‘yan majalisar da suka goyi bayan nasa sun haɗa da Hon. Emmanuel Agbaje, na mazaɓar Akoko-Edo ta biyu da Hon. Nosayaba Okunbor na mazaɓar Orhiomwon ta gabas, da Hon. Dumez Ugiagbe, zaɓaɓɓen mamba mai wakiltar mazaɓar Arewa maso gabashin Ovia ta ɗaya da kuma Mr. Hon. Vincent Uwadiae, zaɓaɓɓen ɗan majalisa mai wakiltar Arewa maso gabashin Ovia ta biyu.
Dukkaninsu dai sun nuna mubayi’arsu ne ta hanyar kai ziyara gidan Osagie ɗin dake birnin Benin.
A wani ci gaba kuma, tuni ‘yan majalisar suka zaɓi wakilin mazabar Orhionmwon ta biyu, Hon. Roland Asoro domin ya maye gurbin Yekini a mtsayin sabon mataimakin kakakin majalisar.
Yanzu haka dai jami’an tsaro na ci gaba da kai kawo a ciki da wajen majalisar domin tabbatar da cikakken tsaro.